Azima Da Aziza Macizai Ne Hausa Novel Complete – Get Now
Download Azima Da Aziza Macizai Ne - Hausa Novel Document

Download Azima Da Aziza Macizai Ne Complete Hausa Novel Document Now On Your Mobile Device, (Kano, Kaduna, Yola, Jigawa, Lagos, And Other Parts Of The World).
Azima And Aziza Macizai Ne is One of the Popular Hausa Novels in Nigeria. Additionally, The Novel is Written in 2022, by One of the Professional Hausa Novel Writers Momyn Ahlan (Fatima).
Table Of Contents
Download Azima Da Aziza Hausa Novel – Full Information
Full Name: Azima Da Aziza Macizai Ne
Author: Momyn Ahlan
Published Date: March 2022
Author’s Group: Kainuwa Writers Association
Total Pages: 220
Total Words: 88,199
Novel Genre: Epic And Love
File Size: 1.22MB
File Format: PDF
Kadan Daga Cikin Littafin Azima Da Aziza Hausa Novel
“Kin Manta Ba Zaku Iya Kashe Juna Ba? Amma Ke Zaki Iya Kashe Azima! Duba Taurarinku Dake Haɗe Ke Kaɗai Aka Yarjema Wa Dan Ki Gani Da Mai Zaki Dakatar Da Azima” a Hankali Aziza Ta Miƙe Ta Kama Bishiya Ta Ɗan Jinginu.
Ta Lumshe Ido, Nan Ta Hau Gane-gane, Tabbas Ba Zasu Iya Kashe Juna Ba Amma Zata Iya Karyawa Azima Kwarin Guiwa, Sannan Wukar Da Ta Yanketa Da Shi Babu Zaren Sakar Dana a Jiki. Aziza Na Ganin Haka Tasa Hannu Ta Shafe Inda Azima Ta Yanketa Nan Wajan Ya Koma Kamar Ba a Taba Saka Ma Shi Wuƙa Ba, Sannan a Ranta Ta Ce.
“Inno Fandi! Yau Inaso Ki Bani Abunda Kika Sha Miƙa Min Ina Ƙin Karba, Ko Ta Wace Hanya Ce Ina So Na Dakatar Da Azima. Inaso Na San Wa Zata Kashe Da Zaren Saƙar Dana Dan Na Basa Kariya. Duk Da Zuciyata Tana Zargin Baffa Azima Take Son Kashewa! Amma Ita Baka Iya Tunanin Abunda Zatayi Dan Komai Ma Zata Iya Yi! Inno Fandi Yau Ina So Ki Bani”.
Aziza a Ranta Take Magana Idonta a Lumshe, Wata Farar Tsohuwa Ce Fara Sosai Tsohuwa Tukuff Ta Bayyanawa Aziza Tana Murmushi Ta Ce “Wani Lokaci Domin Tsaida Zubda Jini! Muma Sai Mun Wanke Hannayenmu Da Jini! Magaji Bawa Ya Ajiye Baiwarsa Yayinda Ya Binnesa. Na Zabi Shiga Jikinki Dan Taimaka Miki Ke Da Mahaifinki a Lokacin Da Na Hango Bala’in Da Zai Faru a Rayiwarku Bayan an Haifeku.
Magaji Ya Yi Tunanin Binne Baiwarsa Zai Ce Wannan Yanki Ta Yi Sanyi, Amma Kashe Banju Shine Babbar Bala’i Ma Wannan Al’karya Dan Yace Zai Dawo. Ba Zaki Iya Jin Komai a Bakina Ba Aziza, Dan Alƙawarin Da Muka Yiwa Magaji Cewa Daga Bakinmu Wani Nasa Ba Zai Ji Tahirihinsa Ba, Sai Dai Idan Shine Ya Bayar, Sabida Alkhairin Da Magaji Ya Mana Ba Zan Manta Da Shi Ba, Hakika Magaji Bawa Jarumi Ne.
Aziza Wannan Abunda Zakiyi Ba Ƙaramin Yaƙi Bane Wanda Ke Daya Ba Zaki Iya Yi Ba. Ni Kuwa Bazan Iya Tayaki Ba, Amma Ga Wannan Ki Ɗora Shi a Ɗamtsen Hannunki Zai Taimaka Miki Sosai. Sa’annan Karki Taba Rabuwa Da Shi Dan Wani Sirhitaccen Karfi Ne, Duk Sadda Kike Bukatar Taimakona Ki Kirani Zan Zo!”
Tana Shirin Bacewa Da Sauri Aziza Ta Ce
“Inno Fandi! Jejin Lore! Ina So Naje” Zaro Ido Inno Fandi Ta Yi Ba Tare Da Ta Yiwa Aziza Magana Ba Ta Bace. A Hankali Aziza Ta Buɗe Ido Ta Kalli Azima Wacce Har Yanzu Take Tsaye Take Magana a Kan Zata Kashe Aziza.
Ɗora Zaren Da Inno Fandi Ta Bata Ta Yi a Damtsen Hannunta Sannan Ta Juya Baya Ta Rintse Ido Nan Fatar Jikinta Ya Hau Sabulewa. Alama Ce Na Zata Koma Macijiya, Nan Ta Zama Wata Katuwar Macijiyafiye Da Yadda Take Zama a Da, Fara Sol Sai Kyalli Take Yi.
Azima Dake Ta Zuba Tin Dazu Bata San Abunda Ke Faruwa a Bayanta Ba, Sai Bayan Da Ta Gama Maganarta Na Karshe Da Fadin “Sai Fa Hakuri! Amma Yau Za Ki Mutu! Ni Haka Nake! Muguwa Ce Ni! Ban San Sani Ba! Ban San Sabo Ba!”
Tana Gama Faɗi Ta Juyo Dan Cakawa Aziza Wuka Nan Ta Ga Babu Aziza, Ɗaga Kan Da Zata Yi Ta Hangi Kanta a Can Sama, Aziza Ta Zama Katuwar Macijiya Mai Cike Da Tsoro Da Firgici, Da Mugun Tsoro Azima Ta Ja Da Baya Tana Fadin “Ya Haka?” Bata Ankare Ba Ta Ji Anyi Sama Da Ita an Yi Kasa Da Ita. Kafin Ta Girgije Ta Ji an Dauketa Ana Zagaye Iska Da Ita, Sai Da Aka Wujijjigata Sosai Sannan Aka Yi Wulli Da Ita, Faɗuwa Ta Yi Ta Bugu.

Ta Bangaren Azima Ko Kaɗan Bata Yi Wankan Sallah Ba Bare Shigar Sallah, Haka Ranar Sallar Ta Wuni Tana Jin Haushin Kowa,kiris Ya Rage Abincin Sallar Ma Bata Watsa Masa Dafi Ba. Dan Haka Kawai Ta Ga Kowa Na Murna Da Farinciki Ita Kuma Tana Ji Kamar Zuciyarta Ya Fashe Da Baƙin Ciki Da Takaici. Haka Aka Gama Cin Sallah Azima Bata Yi Shigar Sallah Ba Illa Kayan Fulaninta Da Ta Dinga Yawo Da Shi Har Satin Sallah.
Bayan Komai Ya Daidaita Haka Rayuwa Ta Ci Gaba Da Tafiya. Bayan Sallah Da Sati Biyu Aziza Ta Fara Zuwa University Din Su Sultana, Bata Shiga Hidimar Kowa Kasancewar Tasan Ita Din Ba Mutum Ba Ce. Haka Zata Je Ta Dawo, Idan Kuma Sultana Na Da Paper Su Kan Je Tare Su Dawo Tare, Tana Nan Tana Tara Kuɗinta Har Ma Da Wa Inda Ta Samu Da Sallah Dan Tace Kwanan Nan Zata Bar Gidan.
“Innalillahi Wa Inna Ilayhirrajiun! Dan Allah Jauro Ka Taimakawa Ƴata Kar Mayyar Nan Ta Kasheta!” Ya Faɗa Yana Mai Riƙe Kafar Jauro, Jauro Ya Ce “Wlh Malam Halliru Na Kasa Yiwa ‘yarka Magani, Wannan Mayyar Tana Da Taurin Kai” Salti Dan Gidan Jauro Ya Ce “Wlh Baffana Baya Da Baiwa Irinta Baffa Magaji, Dama Wajan Baffa Magaji Kuka Je Da Yanzu Ta Samu Sauki, Amma Ku Fara Zuwa Kuyi Kamun Kafa Da Sarki Chubaɗo”
“Wlh Zanci Ubanka Salti! Zaka Fita Mini Ka Bani Waje Ko Sai Na Bazar Da Kai Da Sanda?” Salti Ya Miƙe Yana Kunkuni Yana Fadin “To Dan Na Fadi Gaskiya Kuma Baffa” Salti Na Fita, Malam Halliru Ya Ce “Hakika Munyi Kuskure, Dole Wajan Magaji Zamu Je Neman Taimako…”
Download Hausa Novels
- Doctor Eesha Hausa Novel
- Abban Sojoji Hausa Novel Complete
- Download Best And Complete Hausa Novels 2022
- Macijine Shi Complete Hausa Novel
- Gidan Uncle Hausa Novel
- Abdulmaleek Bobo Complete Hausa Novel
- List Of Hausa Novels And Websites To Download For Free
- Jarababben Namiji Complete Hausa Novel
- Hausa Novels Cinema
- Tsintacciya Hausa Novel Complete Document
I’m so excited to read this novel!