Aure Kawai Shirme Ne Babu Riba A Cikinsa – Inji Wata Budurwa
Babu Ribar Azo A Gani A Cikin Rayuwar Aure

Aure Kawai Shirme Ne Babu Riba A Cikinsa – Zainab Naseer
A Dai-Dai Lokacin Da Jama’a Ke Fafutukar Nemawa Kansu Abokan Rayuwa. Sai Gashi Wata Baiwar Allah Mai Suna Zainab, Tace ‘Aure Kawai Shirme Ne Domin Babu Riba A Cikinsa’. Matashiyar Yar Gwagwarmaya Wato Zainab Naseer Ahmad Ta Bayyana Hakan Ne A Shafinta Na Sada Zumunta Wato Facebook.
A Dai-Dai Lokacin Da Maza Ke Neman Matan Aure Haka Zalika Matan Ke Neman Mazajen Da Zasu Rikesu Hannu Bibbiyu. Malama Zainab Naseer Ahmad Tace Shi Aure Ba Dole Bane. Asalima Shi Aure Ra’ayine, Da Wadanda Sukayi Da Wadanda Basuyiba Duk Basuda Wani Banbanci. Musamman Ma Ga Mata Da Ake Yawaita Zungurarsu Ana Tambayar Mace, Yaushe Zakiyi Aure? Da Zaran Mace Ta Girma Idan Mutum Ya Aureta, Kawai Sai Ya Ringa Kallon Taimaka Mata Yayi.
Budurwar Ta Bayyana Cewa Aure Shirme Ne, Inda Tace ‘Shi Aure Abu Guda Dayane Kawai Na Rayuwa, Kuma Ba Kowane Zai Iya Wannan Ba. Don Haka A Daina Wasu Maganganu Akan Cewa Wai Dole Sai Anyi Aure’.
Budurwar Ta Kara Da Cewa ‘Ba Wai Kuma Da Mace Tayi Aure Hakan Na Nuni Da Cewa Tafi Wadannan Da Basuyi Bane, A’a, Duk Daya Suke’.
Inda A Karshe Dai Ta Karkare Bayanin Nata Da Cewa Aure Shirme Ne, Domin Babu Wani Riba A Cikinsa.
Kar Kuce Bamu Sanar Muku Ba, Zaku Iya Samun Zafafan Shirye-Shiryenmu A Shafin Hausa Cinema. Litattafan Hausa (Hausa Novels), Wakokin Hausa (Hausa Music), Fina-Finan Hausa (Hausa Videos), Hotunan Hausawa (Hausa Photos), Labaran Hausa (Hausa News), Dama Abubuwan Ilimantarwa Ga Mutanenmu Hausawa (Hausa Education).
Akwai Wani Abu Daka Karu Da Wannan Rahoto Na Jaruma Zainab Naseer Ahmad?